Wane tasiri ne zaɓen Turkiya zai yi ga ƙasashen duniya?
Idan har shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan ya faɗi zaɓe a ranar 28 ga watan Mayu, za a iya samun sauyi na mu’amular ƙasar da ƙasashen duniya.
Ƙarƙashin shugabancin Erdogan, Turkiyya ta fusata aminanta ƙasashen yammani saboda amincinta da Rasha. Ya kuma aike da dakarun Turkiyya a rikicin Iraƙi da Syria da Libya.
Ɗan takarar adawa Kemal Kilicdaroglu, ya yi alƙawalin zama babban mai da’awar muradun ƙasashen yammaci.
Ya Turkiyya za ta yi da ƴan gudun hijirar Syria?
Akwai kimanin ƴan Syria miliyan 3.7 da ke cikin Turkiyya, waɗanda suka gujewa yaƙi a ƙasarsu – da kuma wasu ƴan gudun hijira na wasu ƙasashe kamar Afghanistan.
Shugaba Erdogan ya ce Turkiyya ‘ba za ta iya maganin” adadin ba.
Dukkaninsu da shi da Kemal Kilicdaroglu sun ce suna son farfado da dangantaka da Syria domin mayar da ƴan gudun hijirar ƙasar.
Amma hakan na nufin za su koma rayuwa ƙarƙashin mulkin shugaba Bashar al-Assad.
A wannan watan, kafofin yada labaran Turkiya sun ambato Mr Kilicdaroglu yana cewa “zan mayar da dukkanin ƴan gudun hijira gida idan an zaɓe ni shugaban kasa.”
Ya yi barazanar ficewa daga yarjejeniyar Tarayyar Turai inda Turkiyya ta amince ta kula da miliyoyin ƴan gudun hijirar Syria, domin hana su tsallakawa turai samun mafaka.
Mista Kilicdaroglu ya ce Tarayyar Turai ba ta cika nata sharadin yarjejeniyar ba.
Ta yaya alaƙar Turkiyya da ƙasashen yammaci za ta sauya?
Tun samar da Jamhuriyyar Turkiyya a 1923, akwai aminci tsakaninta da manyan ƙasashen yammaci.
Turkiyya tana daga cikin masu yawan sojoji a NATO, ƙawance tsaro na ƙasashen yammaci. Ta kuma shigar da buƙatar neman shiga EU.
Amma, shugaba Erdogan ya sha bayyana ƙasashen yammaci a matsayin “ƴan mulkin mallaka” ko “marar adalci”
Ƙarƙashin shugabancinsa, Turkiyya ta ƙarƙafa dangantaka da Rasha.
A 2019, ya saye jiragen yakin Rasha samfurin S-400.
Domin mayar da martani, Amurka ta dakatar da Turkiyya daga kungiyar ƙasashe masu samar da jiragen yaƙi na F-35.
Turkiyya kuma ta toshe burin Sweden na shiga NATO bayan Rasha ta abka wa Ukraine, tana cewa Sweden ta taimakawa maƙiyyan Turkiyya.
Idan har aka zaɓi Mista Kilicdaroglu a matsayin shugaban Turkiyya, zai mayar da hankali wajen gyara huldar ƙasar da ƙasashen yammaci, in ji Galip Delay na Chatham House da ke London.
“Zai ƙarfafa hulda da ƙasashen yammaci. Huldar ƙasashen waje za ta yi ƙasa fiye da zamanin shugaba Erdogan.”
Mista Kilicdaroglu ya ce a matsayinsa na shugaba zai sake tsara buƙatar Turkiyya ta shiga EU, kuma zai tabbatar da hukuncin kotun Turai ta kare haƙƙin ɗan Adam ya yi daidai da Turkiyya.
Amma barazanar ficewa daga yarjejeniyar ƙasar da Tarayyar Turai kan kula da ƴan gudun hijirar Syria, ya nuna cewa ya shirya tunkarar manyan ƙasashen yammaci.
Ta yaya manufofin Turkiyya kan Ukraine za su sauya?
Turkiyya na son zama tsakiya kan hulɗarta da Rasha da kuma Ukraine tun soma yaƙin.
Ta ƙi ƙaƙaba takunkumin ƙasashen yammaci kan Rasha, amma ta sayar da jiragenta ga Ukraine.
Turkiyya kuma ta kasance mai shiga tsakani a yarjejeniyar fitar da hatsi daga Ukraine ta Bahar Aswad zuwa ƙasashen duniya.
Idan Mista Kilicdaroglu ya zama shugaba, ba zai fi ba Rasha fifiko ba, in ji Hamdullah Baycar na Jami’ar Exeter.
“Ba zai yi wannan amincin ba na kud-da kud,” in ji shi. “Amma kuma ba zai zama maƙiyin Rasha ba.”
Ta yaya alaƙar Turkiyya da ƙasashen Gabas Ta Tsakiya za ta sauya?
A Libya, dakarunta na goyon bayan gwamnatin hadaka – da ke da cibiya a Tripoli – da ke fada da dakarun da Janar Haftar ke jagoranta a gabashi.
“Turkiyya tsohuwar aminiyyar Libya ce kuma tana son abubuwa su daidaita,” in ji Dr Begum Zorlu ta Jami’ar London.
A Iraƙi da Syria, Dakarun Turkiyya na adawa da mayaƙan da ake kira YPG da kuma mayaƙan PKK waɗanda aka ayyana a matsayin ƴan ta’adda a Turkiyya da wasu ƙasashe.
Gwamnatin Turkiyya na zargin YPG da goyon bayan PKK.
Wannan ya fusata Amurka, da ke ɗaukar YPG a matsayin ɗaya daga cikin aminanta a Syria.
Mista Kilicdaroglu ya ce a matsayinsa na shugaba, zai tabbatar da manufar ƙasashen waje ta kaucewa shiga tsakani.
Amma babu tabbas ko zai janye dakarun Turkiyya daga Iraƙi da Syria da Libya.
“Akwai ƴan kishin ƙasa da dama a ɓangaren Mista Kilicdaroglu na ƙawancen jam’iyyun adawa da za su nuna kin amincewarsu,” in ji Dr Zorlu.
Ta yaya alaƙar Turkiyya da China za ta sauya?
Alaƙar Turkiyya da China ta shafi kuɗi ne da kasuwanci.
Ta shiga ƙawancen China domin inganta kasuwancinta kuma ta karɓo rance daga China.
China ta samarwa Turkiyya da rigakafinta na farko da ta samar lokacin annobar korona.
Gwamnatin Erdogan ta yi taka-tsan-tsan wajen gujewa saɓawa China kuma ta yi shiru kan zargin da ake yi wa China na ƙuntatawa ƴan ƙabilar Uyghurs – duk da ana cewa asalinsu Turkawa ne.
Mr Kilicdaroglu ya ce a matsayinsa na shugaba, zai yi magana game da batun da gwamnatin China.
Ko da yake a cewar Mista Baycar: “Mr Kilicdaroglu yana ɓaɓatu yanzu kan Uyghurs amma idan ya ci zaɓe zai yi gum da bakinsa.”
Ko Turkiyya za ta sauya manufofinta kan Afirka?
Sama da shekaru 20, Turkiyya ta samar da ofisoshin jakadanci a ƙasashen Afrika da dama.
Tana amfani da ƙarfinta mai saussauci a can, inda ta kafa makarantu a sassan nahiyar da samar da tallafin karatu ga ƴan Afrika da ke karatu a Turkiyya.
Ta kuma sayar da kayan yaƙi, kamar jirage marar matuki ga ƙasashen Afrika da dama.
Dr Zorlu ta ce gwamnatin Erdogan tana tasiri a Afrika saboda yana son farfaɗo da martabar Turkiyya a matsayin babbar mai tausayin ƙasashe matalauta.
“Shugaba Erdogan na son haɗa kan ƙasashe waɗanda ke ganin ƙasashen yammaci sun yi watsi da su,” in ji ta.
Amma ta ce manufofin Turkiyya ga Afrika akwai alamun za su ci gaba da tabbata ko da kuwa an samu sauyin shugabanci.